Sharhin Littafin Arabaeenan Nawawi - Gabatarwa

SHARHIN
LITTAFIN HADISIN
ARBA’EENAN-NAWAWI
(شرح الكتاب الأربعين النووية)
Na
Nana A’isha Muhammad



 GABATARWA
Godiya ta tabbata ga Allah (S.W.T.), Mahaliccin kowa da komai, tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabinmu Habibinmu Abin koyinmu Muhammad (Salaawatullahi alayhi) da alayensa da sahabbansa adalai da wadanda suke koyi da bin tafarkinsa har izuwa ranar sakamako.

Hakika Allah Madukakin Sarki Yana cewa a cikin Alkur’ani, Suratul Juma’a aya ta 2:

 هُوَ ٱلَّذِى بَعَثَ فِى ٱلۡأُمِّيِّـۧنَ رَسُولاً مِّنۡہُمۡ يَتۡلُواْ عَلَيۡہِمۡ ءَايَـٰتِهِۦ وَيُزَكِّيہِمۡ وَيُعَلِّمُهُمُ ٱلۡكِتَـٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَإِن كَانُواْ مِن قَبۡلُ لَفِى ضَلَـٰلٍ مُّبِينٍ ۝
“Shi ne (Allah) Wanda Ya aika, a cikin mabiya al’adu (marasa rubutu da karatu), wani Manzo daga gare su yana karanta ayoyinSa a kansu, kuma yana tsarkake su, kuma yana sanar dasu Littafin da hikima ko da yake sun kasance daga gabaninsa lallai suna a cikin bata bayyananne”.

Bayan saukar da Alkur’ani da Allah Yayi ga zababben wannan al’ummar (wato Annabi Muhammad S.A.W.) [e.g. Musnad Ahmad: 13,909]. Sai kuma Allah Ya bashi iko da dama da zai yiwa al’ummar bayanin dukkan abin da ya shafi addini da rayuwa wahyan da hikiman (Hikima itace ‘Sunnah’ in ji Imam Ash-Shafi’i) [Qur’an: Saf: 9], ta hanyoyi da suka hada da ya aikata (فعل) sai kwaikwayeshi, ko ya bada umarni (أمر) sai a bi, ko ya hana (نهي) sai a hanu, ko a yi a gabansa bai yi magana تقرير (bai ce a daina aikatawa ba), to ruwaito wadannan abubuwan shi ake cewa Hadisi a wajen malaman hadisi a takaice.

Hadisi kuwa, indai ya tabbata ingantacce daga Manzon Allah (S.A.W.) ba mu da kokwato cikinsa cewa tabbatas Allahne Ya kunsawa Annabi (S.A.W.) domin ya isarwa mutane da wani sako saboda shi Annabi (S.A.W.) baya fadin son ransa face wani wahayi da aka masa, kuma an sanya mana shi (Annabi) ya zame mana abin koyi [Nisa’i: 59; Nahl: 44; Ahzab: 21;Najm, aya ta 3-4].

Za mu fahimci cewa; Hadisi a wajen Musulmai shi ne madogara ta biyu bayan Alkur’ani da ake duba izuwa gareta domin kara fahimta ko warware wata mas’ala a cikin addini ko wani bangare na rayuwa, ko neman karin bayani akan abin da bai fito karara a Alkur’ani Maigirma baو duba izuwa ga matn (abin da hadisin ya kunsa) da kuma sanadi (silsilar yadda aka sami hadisin).

Ilimin sanin hadisi kuwa fagene mai fadi da malamai suka yi bayaninsa dalla-dalla wanda ya kunshi bangaro kamar haka: Usulul Hadis, Mustalahul Hadis, ‘Ilm riwaya wad-dirayatl Hadis, al-Jarh wa’l-ta’dil,’ilm rijal (‘ilm tarikhul riuwat, ma’rifat awtan al-ruwat wal biladihim, ma’rifat al-mu’talif wal-mukhtalif minal asma wa-ansab) da sauransu. Daga nan zaka ji an bawa hadisi wani suna Mutawatir, Ahad, Gharib, ‘Aziz, Mashhur (ta bangaren adadin wadanda suka ruwaici hadisi). Ko kuma Mudallas, Musalsal (ta yanayin da aka ruwaito hadisin). Ko kuma Shadh/Shazzi, Munkar, Mudraj (ta yanayin Matn da Isnadin hadisi). Ko kuma Mudtarib, Maqlub, Ma’lul/Mu’allal (ta yanayin boyuwar wani abu cikin matn ko isnad). Ko kuma Sahih, Hasan, Da’if, Maudu’ (ta yanayin rawi, al-thiqat dss).

Daga cikin Dukkan wadannan ilmai ba za su koyo ba a kankanin lokaci ko social media ba, dole sai mutum ya koma wajen malamai yardaddu masana ilimin sosai yana bibiyarsu tukun mutum zai kamtafa daga koramunsu, Allah Ya sa mu dace.
Wannan dan takaitacce rubutune akan Sharhi littafin Hadisai na Imam an-Nawawi wato Arba’una ko Arba’eena Hadisi, ko Arba’eenan Nawawi cikin harshen Hausa tare da takaitaccen nazari da alakanta hadisan cikin ibada, aqeeda, mu’alama da sauran bangarorin addini da kuma rayuwa. Ina rokon Allah Ya dafa min na rubuta daidai, Ya kuma tsare ni da rubuta kuskure ko son zuciya wajen bayani, Ya sakawa iyaye da kuma malamaina da alkhairi, amin.


Nana A’isha Muhammad
30th Muharram, 1439AH
21st October, 2017CE

Comments

Popular posts from this blog

Tarihin Sahabbai Mata 1: Maimunatu bint al-Harith (R)

Sahabbai 12 da aka fi ruwaito hadisan Annabi S.A.W. daga garesu

Tarihin Sahabbai 10: 1. Muaz bin Jabal (R)